Kungiyoyi 9 sun samu nasarar kaiwa zagayen gasarzakarun Turai na 2
Kungiyoyi 9 ne a yanzu haka suka samu nasarar kaiwa zagayen gasar zakarun Turai na 2 da ya kunshi adadin kungiyoyi 16.
Wallafawa ranar:
Kungiyoyin kuwa sun hada da Barcelona, Bayern Munich, Borussia Dortmund, Chelsea, FC Porto, Sevilla, Juventus, Liverpool da kuma Manchester City.
Dangane da yin zarra wajen zura kwallaye a raga kuwa, bayan kammala wasanni 5 na matakin rukunin gasar zakarun Turan, ‘yan dake kan gaba sun hada da Alvaro Morata na Juventus, Haaland na Dortmund, da kuma Marcos Rashford na Manchester United dukkaninsu da kwallaye shida-shida.
Sauran dake biye da yawan kwallayen sun hada da Berisha na Salzburg, Giroud na Chelsea, da Plea na kungiyar Borussia Moenchengladbach dukkaninsu da kwallaye biyar-biyar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu