Super Falcons ta Najeriya ta lashe kofin WAFU
Kungiyar kwallon kafar Najeriya bangaren mata Super Falcons ta yi nasarar lashe gasar cin kofin kasashen yammacin Afrika da ya gudana a Ivory Coast bayan lallasa mai masaukin baki a wasan karshe da kwallaye 5 da 4.
Wallafawa ranar:
Yayin wasannin gasar da ta gudana tsakanin kasashen 8 na yankin yammacin Afrikan, Super Falcons ta kafa tarihin kammala wasannin ba tare da ta yi rashin nasara a hannun kowacce kungiya ba.
Tuni dai shugaban Najeriyar Muhammadu Buhari ya aikewa tawagar da sakon taya murnar lashe kofin, inda ya bukace su da ci gaba da nuna hazaka a wasannin gasar cin kofin duniya da ke tafe cikin shekarar nan a Faransa, gasar da tuni Super Falcons ta samu tikitin zuwanta, tun bayan dage kofin Afrika watannin baya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu