Mikel Obi ya soke kwantiraginsa a China
Dan wasan Najeriya, John Mikel Obi ya soke kwantiraginsa da kungiyar kwallon kafa ta Tianjin Teda da ke buga gasar Lig ta China.
Wallafawa ranar:
Yanzu haka dan wasan na tsakiya zai raba gari da kungiyar duk da cewa, akwai sauran sama da kwantiragin shekara guda akan sa.
Mikel bai shiga cikin tawagar Tianjin ba wadda ta yi balaguro zuwa Spain don samaun horan bude fagen shiga sabuwar kaka.
A yayin zantawa da manema Labarai, dan wasan na Super Eagles ya ce, kawo yanzu bai tsayar da shawarar in da zai koma ba, amma akwai yiwuwar ya koma nahiyar Turai ko kuma ya ci gaba da zama a China a cewarsa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu