Isa ga babban shafi
Wasanni

Ban ji dadin yadda nahiyar Afrika ta gaza a Rasha ba - Infantino

Shugaban hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA Gianni Infantino, ya ce bai ji dadin yadda nahiyar Afrika ta gaza samun mai wakiltar ta ba, a zagayen gaba da na rukuni a gasar cin kofin duniya ta bana da ke gudana a Rasha.

Shugaban hukumar FIFA, Gianni Infantino.
Shugaban hukumar FIFA, Gianni Infantino. REUTERS/Jorge Adorno
Talla

Kalaman na Infantino sun zo ne, bayan da dukkanin kasashe biyar, da suka hada da Najeriya, Morocco, Tunisia, Senegal da Masar, masu wakiltar nahiyar ta Afrika, suka fice tun a zagayen farko na gasar a matakin rukuni.

Karo na farko kenan da kasashen nahiyar Afrika suka gaza kai wa zagaye na gaba daga matakin rukuni a gasar cin kofin duniya, tun bayan irin haka da ya taba aukuwa a shekarar 1982.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.