Isa ga babban shafi
wasanni

Ana bincike kan barazanar kashe golan Liverpool

Rundunar ‘yan sandan Merseyside ta ce, tana da masaniya game da barazanar kisan da aka yi wa mai tsaren ragar Liverpool, Loris Karius bayan kammala wasan karshe tsakaninsu da Real Madrid a gasar cin kofin zakarun Turai.

Mai tsaren ragar Liverpool Loris Karius ya bai wa magoya bayan kungiyar hakuri
Mai tsaren ragar Liverpool Loris Karius ya bai wa magoya bayan kungiyar hakuri REUTERS
Talla

An yi wa golan barazanar hallaka shi da iyalansa saboda kura-kuran da ya yi har aka zura musu kwallaye 2 a wasan wanda Madrid ta samu nasara da kwallaye 3-1.

Rundunar ‘yan sandan ta ce, tana gudanar da bincike game da barazanar wadda aka yi ta shafukan sada zumunta.

Karius mai shekaru 24 kuma dan asalin kasar Jamus, ya bai wa magoya bayan Liverpool da sauran ‘yan kungiyarsa hakuri kan kura-kuransa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.