Isa ga babban shafi
Wasanni

Najeriya tana da zakakuran 'yan wasa - Simeone

Mai horar da kungiyar Atletico Madrid Diego Simeone, ya ce tawaga ta 2 ta ‘yan wasan Najeriya Super Eagles ta kunshi kwararru da zasu iya buga wasanni a manyan kungiyoyin kwallon kafa da ke nahiyar turai.

Mai horar da kungiyar Atletico Madrid Diego Simeone.
Mai horar da kungiyar Atletico Madrid Diego Simeone. REUTERS/Juan Medina
Talla

Simeone ya bayyana haka ne bayan kammala wasan sada zumunci tsakanin ‘yan wasansa na Atletico Madrid da Najeriya inda suka samu nasara ta kwallaye 3-2, a filin wasa na Godswill Akpabio, da ke garin Uyo, na jihar Akwa Ibom.

Kocin na Atletico Madrid ya ce bayyana wasan da mai horarwa na Super Eagles Salisu Yusuf ya jagoranta da cewa ba wasa ne mai sauki ba, wanda ya kagu a kammala saboda fargabar yin rashin nasara a hannun ‘yan Najeriyar.

‘Yan wasan Najeriya Usman Mohammed da Kelechi Nwakali ne suka ci wa Super Eagles kwallayenta 2, yayinda Angel Correa, Fernando Torres da Borja Garces suka ci wa Atletico Madrid kwallaye 3.

A makon da ya gabata ne Atletico Madrid ta lashe kofin gasar Europa, bayan lallasa Marseille da kwallaye 3-0.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.