Isa ga babban shafi
wasanni

Na fi son lashe kofin zakarun Turai fiye da komai- Salah

Dan wasan gaba na Liverpool, Mohamed Salah ya ce, lashe kofin gasar zakarun Turai ya fi muhimmanci a gare shi fiye da duk wata kyauta da zai lashe shi kadai a kakar bana.

Mohamed Salah ya jefa kwallaye 40 a cikin wannan kaka
Mohamed Salah ya jefa kwallaye 40 a cikin wannan kaka Reuters/Lee Smith
Talla

Kawo yanzu dai, Salah, dan asalin Masar kuma mai shekaru 25, ya jefa kwallaye 40 a raga a cikin wannan kaka, yayin da kuma ya lashe kyautar gawarzon dan wasan firimiyar Ingila na wata-wata sau uku, kuma shi ne dan wasa na farko da ya lashe kyautar sau uku a kaka guda.

Salah ya lashe kyautar a cikin watannin Nuwamba da Fabairu da kuma Maris da suka gabata.

Sai dai dan wasan ya ce, daukan kofin zakarun Turai a bana, shi ne mafi muhimmanci a gare shi fiye da duk wata kyauta.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.