Wenger na dakon makomarsa a Arsenal
Mai horar da kungiyar kwallon kafa ta Arsenal Arsene Wenger ya gana da mai kungiyar Stan Kroenke, a yayin da ake dakon sanin makomarsa ta ci gaba da horar da kungiyar ko kuma raba gari da ita.
Wallafawa ranar:
Babu dai cikakken bayani dangane da sakamakon ganawar tasu, amma ana saran sanar da matakin da za a dauka kan Wenger a taron Darektocin kungiyar a wannan Talata.
A wannan kakar ne kwantiragin Asrene Wenger zai kare bayan ya jagoranci kungiyar na tsawon shekaru 21.
Rahotanni sun ce, Kocin na son ci gaba da zama a kungiyar, amma yana fuskantar matsi da caccaka saboda halin da Arsenal ta tsinci kanta a ciki, musamman na rashin samun gurbi a gasar zakarun Turai a kaka mai zuwa, bayan ta kammala gasar Premier ta Ingila a mataki na biyar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu