Wasanni-Najeriya
Bahagon ‘Yan sanda ya yi kisa
Manyan wasanni uku aka fafata a wasan damben gargajiya da aka yi a gidan Umaru Fiyalu da ke jihar Kaduna a tarayyar Najeriya a yammacin ranar Asabar.
Wallafawa ranar:
Talla
Cikin damben da aka yi Bahagon ‘Yan sanda daga bangaren Arewa ya doke Dan Shaddadu daga bangaren kudu.
Sai Bahagon Sisco daga bangaren Arewa da ya buge Inda daga bangaren Arewa.
An kuma kara tsakanin Na Masta daga bangaren Arewa da kuma Shagon bata Isakka daga bangaren kudu, inda aka tashi babu kisa a tsakani.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu