PSG na barazana ga Real Madrid
Cocin Real Madrid Rafael Benitez ya bayyana cewa an jefa kungiyarsa a cikin rukunin kungiyoyi mai wahala a gasar cin kofin zakarun nahiyar Turai, inda ya ce Paris PSG ta Faransa, ita ce babbar barazana a gare su a cikin wannna rukunin
Wallafawa ranar:
Real Madrid ta fada cikin rukunin A, wanda ya hada da PSG da Shaktar Donetsk ta Ukraine da kuma Malmo ta kasar Sweden.
A cewar Benitez wannan rukunin ba mai sauki bane kuma sun san PSG babbar Kungiya ce mai zaratan yan wasa wadda kuam ke karfafa kanta a duk kakarwasanni.
A jiya ne hukumar kwallon kafar Turai ta fitar da rukunnan kungiyoyin da zasu fafata a gasar cin kofin zakarun nahiyar Turai.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu