Isa ga babban shafi
Marathon

Bekele ya lashe tseren Marathon a Paris

Dan kasar Habasha, Kenenisa Bekele ne ya lashe teren gudun Marathon da aka gudanar a birnin Paris a jiya Lahadi bayan ya yi gudun kilomita 42.195 cikin sa’oi biyu da minti 5 da dakika 4 a kewayen Paris.

Kenenisa Bekele na Habasha a tseren gudun Marathon karo na 38 da aka gudanar a Paris
Kenenisa Bekele na Habasha a tseren gudun Marathon karo na 38 da aka gudanar a Paris Reuters/Gonzalo Fuentes
Talla

Abokin gudunsa na Habasha Limenih Getachew ya zo a matsayi na biyu, yayin da kuma Luka Kanda na Kenya, ya zo a matsayi na uku.

A bangaren mata ‘Yar tseren gudun kasar Kenya Flomena Cheyech ce ta lashe tseren gudun na Marathon. ‘Yar kasar Habasha Yebrgual Melese ce a matsayi na biyu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.