Kwallon Kafa
Wenger yace yana bukatar V. Persie ci gaba da taka kwallo a Arsenal
Kocin Arsenal, Arsene Wenger ya bayyana fatar ganin Robin Van Persie ya ci gaba da taka kwallo da kungiyar bayan dan wasan ya nemi ficewa daga Arsenal.
Wallafawa ranar:
Talla
Tuni dai Manchester United da Manchester City da Juventus suka bayyana bukatar dan wasan.
Sai dai Arsene Wenger yace Van Persie fitaccen dan wasa ne a duniya kuma Arsenal tana bukatar abunta.
A yau ne dai ake sa ran Arsenal zata kara da Malaysian XI, kafin ranar Jum’a ta kece raini da Manchester City a birnin Beijing na kasar China.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu