Isa ga babban shafi

Faransa ta karrama Malamin da wani dan ta'adda ya kashe a makaranta

Daukacin al'ummar Faransa sun karrama Malamin mai shekaru 57 Dominique Bernerd, da wani dan ta'adda ya kashe tare dajikkata wasu, lokacin wani hari da kai da wuka a wata makaranta da ke yankin Arewa maso Yammacin kasar.

Wurin da masu alhini ke ajiye furanni don karrama Malamin
Wurin da masu alhini ke ajiye furanni don karrama Malamin © france 24
Talla

Harin da yayi sanadin mutuwar Malamin ya daga hankalin daukacin al’ummar Faransa, ciki har da shugaba Emmanuel Macron.

Kasar dai ta tsaurara matakan tsaro bayan da maharin ya aikata aika-aikar, a yayin da tuni gwamnati ta baza dakarun tsaro dubu 7 a sassa daban daban don tabbatar da tsaro.

Harin na Arras wani gari da ke dauke tarin Yahudawa da al’ummar Musulmi,  sunyi alhini da Allah wadai  da rikicin da ake gwabzawa a Gaza.

Jami’an tsaro dai sun cafke wanda ake zargi da danyen aikin mai shekaru 20 kuma dan kasar Rasha da ya halaka malamin tare da jikkata wasu uku a makarantar da yake halarta.

Kamfanin Dillancin Labaran Faransa AFP ya bayyana cewa  wadanda suka jikkatan yanzu haka sun fara murmurewa a asibiti.

Daukacin makaranrun da ke Faransa sun yi shiru na minti daya domin nuna alhini da kisan gillar da aka yiwa Malamin.

Malamin dai ya ci karo da dan ta'addan ne a yayin da ya shiga matarantar da yake aiki kuma ya daddaba masa wuka a ranar Juma'ar da ta gabata.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.