Isa ga babban shafi

Adadin wadanda suka mutu a girgizar kasar Turkiya da Syria ya zarta dubu 11

Masu aikin ceto a Turkiyya da Siriya dake fama da tsananin sanyi na ci gaba da aikin gano masu sauran numfashi a karkashin gine-ginen da girgizar kasar ta rutsa da su , yayin da adadin wadanda suka mutu ya zuwa yanzu ya haura dubu 11.

Yadda masu aikin ceto ke zakulo masu sauran numfashi a karkashin baraguzai a wani yankin Turkiya bayan girgizar kasa.
Yadda masu aikin ceto ke zakulo masu sauran numfashi a karkashin baraguzai a wani yankin Turkiya bayan girgizar kasa. AP - Khalil Hamra
Talla

Girgizar kasar mafi muni da kasashen suka gani cikin shekaru da dama ya kara haifar da tabarbarewar al’umara a yankin kan iyakar da dama can ke fama da rikici, yayin da wadanda suka tsari daga iftila’in da yanzu haka ke rayuwa a kan tituna ke kona tarkace a kokarinsu na samun dumi saboda tsananin sanyi gami da dusar kankara.

Yayin da taimakon kasashen duniya suka fara isa, masu aikin ceto na kokarin zakulo masu sauran numfashi, kuma cikin nasarar da suke samu ana ganin abubuwan al’ajabi da ban tausai, ciki harda yadda aka ciro wani jariri da rai daga baraguzan gine-gine a Siriya, wanda alamu suka nuna cewa ba’aji da haihuwarsa ba saboda ko cibiyarsa na hade da ta mahaifar sa wacce ta mutu.

Shugaban kasar Turkiyya Recep Tayyip Erdogan ya ayyana dokar ta baci na tsawon watanni uku a larduna 10 da lamarin yayi kamari.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.