Isa ga babban shafi
Amurka-China

Biden ya gargadi China a kan illolin taimaka wa Rasha a yakinta da Ukraine

Shugaban Amurka  Joe Biden ya gargadi takwaransa na China  Xi Jinping a kan illolin taimaka wa Rasha a yakin da take da Ukraine, a yayin da Chinar har yanzu bata nuna alamun bin sahun sauran kasashen duniya wajen yin Allah wadai da Rasha ba.

shugaban Amurka Joe Biden.
shugaban Amurka Joe Biden. REUTERS - TOM BRENNER
Talla

Fadar White House ta ce Biden ya yi wa shugaba Xi bayani ne a game da rashin alfanun taimaka wa Rasha da kayayyakin yaki a yayin da take yin dirar mikiya a kan  biranen Ukraine da fararen hula.

Sanarwar Fadar gwamnatin Amurka na zuwa ne bayan ganawa ta sa’o’i biyu da shugabannin suka yi ta wayar tarho a jiya Juma’a.

Sai dai China ba ta bayyana takamammen matsayinta ba bayan ganawar, inda tashar talabijin kasar ta ruwaito shugaba Xi yana cewa, babu abin da wanna yaki zai tsainana wa kowa, ayayin da babu wani bayani a game da caccakar Rasha.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.