Isa ga babban shafi
faransa

An fara bincike kan zargin fyade a fadar Macron

Masu gabatar da kara a Faransa na ci gaba da bincike kan zargin da ake yiwa wani soja da yiwa abokiyar aikin sa Fyade a fadar shugaban kasar, abinda ake ganin ka iya shafawa gwamnatin shugaba Macron kashin kaji.

Fadar shugaban kasar Faransa ta Elysee yayin wani bukin al'adu
Fadar shugaban kasar Faransa ta Elysee yayin wani bukin al'adu © Ian Langsdon/Pool via Reuters
Talla

Bayanai sun ce lamarin ya faru ne jim kadan bayan da shugaban Kasar Emmanuel Macron ya bar wajen taron karrama manyan sojojin kasar tun a watan Yulin da ya gabata.

Sojojin biyu dai na cikin wadanda aka tura don tabbatar da tsaro a fadar shugaban kasar a ranar, a lokacin ne kuma sojan ya hilaci abokiyar aikin sa tare da yi mata Fyaden.

Sojan da ake zargi dai ya aikata laifin ne a ranar 12 ga watan Yulin da ya gabata, sai dai kuma an bukaci da ya rika ci gaba da amsa tambayoyin jami’an tsaro duk da cewa a baya ba’a gurfanar da shi gaban kotu a hukumance ba.

Fadar shugaban Faransa dai na kokari wajen ganin cewa abin kunya bai fita ta bangaren gwamnati ba, amma da alama hakan bata yiwuwa don kuwa ko a baya-bayan nan ma kotu ta yankewa wani dogarin Shugaba Macron Hukuncin daurin shekaru 3 sakamakon naushin wani cikin masu zanga-zanga a watan Mayun 2018.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.