Isa ga babban shafi
Turkiya

Rikicin kan iyaka bai hana Turkiya cigaba da neman gas a tekun Meditereniya ba

Kasar Turkiya ta cigaba da aikin neman iskar gas a cikin tekun Meditereniya da kuma bada umurnin cigaba da atisayen sojin ruwa, yayin da takaddama tsakanin ta da kasashen Girka da Faransa ke dada tsami saboda hako makamashin da kuma rikicin iyaka.

Jirgin ruwan Turkiya dake binciken hako arzikin iskar gas a tekun Mediteraniya (daga tsakiya) tare da rakiyar jiragen yaki. 12/8/2020.
Jirgin ruwan Turkiya dake binciken hako arzikin iskar gas a tekun Mediteraniya (daga tsakiya) tare da rakiyar jiragen yaki. 12/8/2020. Turkish Defense Ministry handout via AFP Photo
Talla

A nata bangaren Girka ta sanar da kulla yarjejeniyar teku da kasar Masar, matakin da Turkiya ke adawa da shi saboda arzikin dake iyakokin kasashen biyu.

Ya zuwa jiya babu wata kasa tsakanin Turkiya da Girka dake nuna alamar sassautawa, yayin da kungiyar kasashen Turai ke kokarin ganin ta sanya bangarorin biyu sun hau teburin tattaunawa domin sasanta rikicin.

Tun a ranar laraba, 26 ga watan Agusta, Girka ta sanar da shirin kaddamar da atasayen soji na hadin gwiwa tare da Faransa, Italiya da Cyprus, a gabashin Meditereniya, yankin mai arzikin Iskar Gas da ake tankiya akai, tsakanin Turkiya, kasar ta Girka da kuma manyan kasashen Turan.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.