Isa ga babban shafi
Faransa

Ministan Cikin Gidan Faransa na dab da murabus

Ministan Harkokin Cikin Gidan Faransa, Gerard Collomb ya sanar da shirinsa na ajiye mukaminsa bayan zaben Majalisar Dokokin Tarayyar Turai a shekara mai zuwa, matakin da zai dada haifar da cikas ga gwamnatin shugaba Emmanuel Macron.

Shugaban Faransa Emmanuel Macron da Ministan Cikin Gidan Kasar Gérard Collomb
Shugaban Faransa Emmanuel Macron da Ministan Cikin Gidan Kasar Gérard Collomb Alberto PIZZOLI / AFP
Talla

Collomb da ke cikin manyan ministocin Macron na gaban-goshi ya shaida wa mujallar L’Express cewa, zai yi murabus don samun damar takarar neman kujerar magajin garin birnin Lyon da ke kudancin Faransa a shekarar 2020.

Collomb ya ce, duk da dai akwai sauran lokacin gudanar da zaben kananan hukumomi, amma akwai bukatar samun isasshen lokacin gudanar da yakin neman zabe.

Collomb mai shekaru 71 ya taba rike mukamin magajin garin birnin Lyon, in da ya shafe tsawon shekaru 16 kan karaga har sai da Macron ya nada shi Minista.

Wannan na zuwa ne makwanni uku da murabus din Ministan Muhallin kasar mai farin jini, Nicolas Hulot, lamarin da ya sosa ran gwamnatin shugaba Macron wanda karbuwarsa a idon Faransawa ta ragu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.