Isa ga babban shafi
Faransa

An gurfanar da Marine Le Pen a gaban kotu

Bangaren shari’a a Faransa ya shigar da karar shugabar Jamiyar National Front Marine Le Pen bisa  zargin yada hotunan da ba su dace ba ta kafar sadarwan Tweeter.

Marine Le Pen, shugabar jam'iyyar Front National
Marine Le Pen, shugabar jam'iyyar Front National Fuente: Reuters
Talla

Matakin da masu shigar da kara a Nanterre, da ke wajen birnin Paris ya biyo bayan da Majalisar kasar ta Faransa ta dauka ne a watan Nuwambar  da ya gabata inda ta cire rigar kariya  na wakiliyar majalisar saboda baza hotunan 3  a shekara ta 2015 na ayyukan ‘yan taadda na IS

 

A  zaben bara dai Shugaban Faransa Emmanuel Macron  ya doke Marine Le Pen, lokacin da ta kara da shi a zaben shugabancin kasar.

Ana zargin ta da laifin yada hotunan ta’addanci da na batsa da ake ganin suna da hatsari ga mutane kasar.

Laifufukan na iya kai ga dauri na tsawon shekaru 3 gidan yari da kuma biyan tara ta kudin Turai Euro dubu 75, kwatankwacin kudin Amurka Dala dubu 91.

Marine Le Pen ta ki amincewa da zargin, inda take cewa da ace wata kasa ce, da har lambar zinari za’a  ba ta saboda ta yada hoton ne domin nuna bakin ciki da ayyukan ‘yan kungiyar IS.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.