Isa ga babban shafi
Faransa

Ana zargin Ministan kasafin kudin Faransa da cin zarafin mata

Masu shigar da kara a Faransa sun yi watsi da wasu zarge-zargen fyade da ake yi wa ministan kasafin kudin kasar Gerald Dermanin, wanda wata mata ta shigar da ta ce lamarin ya faru ne tun a shekarar 2009 lokacin da ta nemi ya taimaka mata wajen goge wasu laifukanta.

Tuni dai Ofishin masu shigar da kara da ke birnin Paris ya kori karar kan Gérald Darmanin, saboda rashin kwararan hujjoji.
Tuni dai Ofishin masu shigar da kara da ke birnin Paris ya kori karar kan Gérald Darmanin, saboda rashin kwararan hujjoji. CHRISTOPHE ARCHAMBAULT / AFP
Talla

Ofishin masu shigar da karar da ke birnin Paris ya ce rashin gamsasssun hujjoji kan zarge-zargen matar ne ya tilasta musu watsi da batun.

Ko da yake dai an yi watsi da wannan batu, amma a bangare guda kuma ministan kasafin kudin na fuskantar wani zargi na daban kan yunkurin yin amfani da matsayinsa don yin lalata da wata mata bisa tilasci.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.