Isa ga babban shafi
Faransa

An samu karuwar 'yan gudun hijira a titunan Paris

Jami’ai a kasar Faransa sun ce yawan ‘yan gudun hijira da ke kwana a kan wasu titunan birnin Paris ya karu, sakamakon rushe sansanin ‘yan gudun hijira na dajin Calais.

Wata 'yar gudun hijira yayin kauracewa sansanin Calais
Wata 'yar gudun hijira yayin kauracewa sansanin Calais Philippe Huguen/AFP
Talla

‘Yan gudun hijirar mafi yawanci ‘yan nahiyar Africa, da suka fito daga Sudan ta Kudu, sun kafa tantunansu ne a gabashin birinin Paris.

Ko da yake ba sabon abu bane ganin zaman ‘yan gudun hijira a yankin, sai dai sun karu a wannan satin daga 1,500 zuwa akalla 2,500.

Shugaban sashin kula da karbar ‘yan gudun hijira na Faransa Pascal Brice yace karuwar masu gudun hijirar a titunan Paris ba yana nufin wadanda aka kwashe daga dajin Calai sun koma wajen da zama bane.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.