Isa ga babban shafi
Britaniya

Britaniya za ta soma karbar yara 'yan gudun hijra

Bayan cimma jituwa Britaniya ta amince ta soma karbar wasu daga cikin yaran dake a sansanin ‘yan gudun hijra a Faransa inda za ta meka su ga danginsu da suka yi nasarar ketarawa kasar

Sansanin 'yan gudun hijra dake Calais na kasar Faransa.
Sansanin 'yan gudun hijra dake Calais na kasar Faransa. Alice Pozycki
Talla

Ana kuma shirin yin hakan nan ne nan ba da jimawa ba bayan cimma jituwa a tsakanin kasashen biyu.

Dubban ‘yan gudun hijra ne dai ke jibge a sansanin Calais dake kasar Faransa da a kullum suke yunkurin shiga Brittaniya dama wasu kasashen nahiyar Turai, akwai kuma yara da dama acikinsu.

Yanzu an soma yiwa yaran da ake ganin danginsu na Britaniya rijista kafin hada su da iyayensu akwai kuma wasu da ake kokarin tantancewa don ganin ko sun cancanci basu mafaka a kasar.

Wannan na zuwa ne a yayin da Faransa ke shirin kulle sansanin na Calais sai dai a daya bangaren Hukumar ‘yan gudun hijra ta Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana fargaba cewar akwai yiyuwar yin fataucin yara.

Daruruwan yara da yaki ya raba da iyayensu ne ke rayuwa a sansanin ba tare da sanin inda iyayensu suke ba.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.