Isa ga babban shafi
Belgium

Wani mutun ya kai harin adda a Belgium

Wani mutun dauke da adda ya raunata jami’an ‘yan sanda mata guda biyu a birnin Charleroi da ke kudancin Belgium.

'Yan sanda sun kashe mutumin da ya kai harn adda kan wasu 'yan sanda mata biyu a kudancin Belgium
'Yan sanda sun kashe mutumin da ya kai harn adda kan wasu 'yan sanda mata biyu a kudancin Belgium FRED DUBOIS / BELGA / AFP
Talla

Rahotanni sun ce, an ji maharin na yin kabbara a lokacin kaddamar da farmakin na yau, kafin daga bisani 'yan sanda su harbe shi har lahira.

Firaministan kasar, Charles Michael ya katse hutunsa da ya ke yi a kudancin Faransa, inda zai koma Belgium don halartar taron tattauna batun tsaron kasar a gobe Lahadi.

Tun lokacin da kungiyar IS ta kashe mutane 32  a birnin Brussels a cikin watan Maris, kasar ta Belgium ta tsaurara matakan tsaro .

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.