Isa ga babban shafi
Faransa

Tarukan gangami domin tunawa da hare-haren da akai wa Faransa

A wannan lahadi ana gudanar da tarukan gangami a sassa daban daban na Faransa domin tunawa da cika shekara guda da mutane sama da milyan 4 suka gudanar da tarukan gangami domin nuna alhini ga harin da aka kai ginin mujallar Charlie Hebdo da kuma wani shagon Yahudawa a kasar.

Tuna harin Charlie Hebdo
Tuna harin Charlie Hebdo RENE-WORMS Pierre/FMM
Talla

A birnin Paris ana kyautata zaton shugaba Francois Hollande da kuma manyan jami’an gwmanatinsa za su halarta taron gangamin na yau a cikin wani yanayi na tsaurara matakan tsaro lura da cewa har kullum kasar na fuskantar barazana daga ayyukan ta’addanci.

Faransa dai ta kaddamar da hare-hare a kan kungiyoyin ‘yan ta’adda musamman a Syria, Iraki da kuma Mali.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.