Isa ga babban shafi
Turai

Kasashen Turai sun tsaurara tsaro a manyan biranensu

Hukumomin Turai sun tsaurara matakan tsaro a manyan biranensu kuma gwamnatocin kasashen sun gudanar da taron gaggawa na ministocinsu a yau Assabar domin tattauna matakan tsaro bayan hare haren da ‘Yan ta’adda suka kai birnin Paris na Faransa.

Shugaban Faransa, François Hollande.
Shugaban Faransa, François Hollande. REUTERS
Talla

Firaministan Birtaniya ya ce zai sake nazari akan tsaron kasa bayan ya gana da ministocinsa.

Shugabannin kasashen Jamus da Italiya da Spain da Austria sun gana da ministocinsu a yau Assabar kan sha’anin tsaro bayan harin Paris.

Ministan harakokin wajen Faransa Laurent Fabius ya ce sun tsaurara matakan tsaro a ofishoshin jekadanci da gine ginen kasar a sassan kasashen duniya, bayan jerin hare haren da ‘Yan ta’adda suka a birnin Paris.

Tun a daren juma’a ne da ake kai hare haren Paris, Shugaba Hollande ya kafa dokar dokar ta-baci a Faransa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.