Isa ga babban shafi
Girka

Wani Dattijo ya tallafawa Girka da kudadensa na Fansho

Wani Dattijo mai shekaru 88 a duniya a Cyprus ya aika wa Firaministan Girka Alexis Tsipras da kudadensa na Fansho kimanin yuro 506 a matsayin gudunmuwarsa ga kasar da ke fama da dinbin bashi.

Hankalin Jaridun Turai ya karkata akan Girka da ta gaza biyan bashin da ake binta
Hankalin Jaridun Turai ya karkata akan Girka da ta gaza biyan bashin da ake binta REUTERS/Jean-Paul Pelissier
Talla

Dattijon ya taimakawa Girka ne da kudadenasa na Fansho domin biyan bashin da ake bin ta.

Dattijon da ake kira Onoufrios Michaelides ya fadi a cikin wasikar da ya aika zuwa Girka cewa ya yi haka ne saboda gamsuwa da matakan da Firaministan ke dauka na kare martabar Girka da al’ummarta.

Dattijon ya bukaci Tsipiras ya ci gaba da kare martabar kasarsa daga manyan kasashe ‘yan jari-hujja.

Dattijon wanda ke sayar da kayan wuta a shagonsa da ke birnin Limassol ya shaidawa Kamfanin Dillacin Labaran Faransa cewa ya yanke shawarar taimakawa kasar Girka ne saboda tausayin mutanen kasar da ya gani a Telebijin suna dogon layi wajen cirar kudi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.