Isa ga babban shafi
Girka

Turai ta ba Girka wa’adi zuwa Alhamis

Shugabannin Kungiyar kasashen da ke amfani da kudin yuro sun ba kasar Girka wa’adi zuwa gobe alhamis domin ta gabatar da sabon shirin biyan bashinta wanda shugabanin za su yi nazari akai ranar lahadi don kaucewa kasar ficewa daga kungiyar.

Firaministan Girka Alexis Tsipras.
Firaministan Girka Alexis Tsipras. REUTERS/Francois Lenoir
Talla

Shugaban Majalisar kungiyar Donald Tusk ya ce wannan shi ne mataki na karshe da za su ba kungiyar.

Shugaban kasar Faransa Francois Hollande ya bukaci hadin kai don warware matsalar Girka.

Kasashen na Turai sun jira Girka ne ta gabatar da sabbin tsare tsarenta a ranar Talata bayan al’ummar Girka sun kada kuri’ar kin amincewa da bukatun ma su bin kasar Bashi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.