An yi zanga-zangar kyamar Musulunci a Jamus
Akalla mutane dubu 18 ne suka shiga wata zanga-zangar nuna kyamar addinin musulunci a birnin Dresde da ke gabashin kasar Jamus. Wata kungiya ce mai suna PEGIDA ta jagoranci gangamin inda ta ce wasu na neman musuluntar da al’ummar Turai.
Wallafawa ranar:
Sai dai masu wannan ra’ayi sun ci karo da turjiya daga wasu Jamusawa masu sassaucin ra’ayi da ke adawa da zanga-zangar a sauran biranen kasar.
Tun a watan Oktoba PEGIDA ke jagorantar zanga-zangar kyamar addinin Musulunci a Jamus duk da shugabar gwamnatin kasar Angela Merkel ta bukaci a dakatar da zanga-zangar.
Shugabannin Kiristoci da ‘Yan kasuwa da shugabannin siyasa a Jamus sun la’anci zanga-zangar da aka gudanar a biranen Berlin da Cologne da Stuttgart da Dresden.
Sai dai kuma masu zanga-zangar sun ci karo da dubban Jamusawa da suka kaddamar da zanga-zangar adawa da masu kyamar Musulunci.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu