‘Yan takarar shugabancin kungiyar tarayyar turai sun fara muhawara
A yau litinin, manyan ‘yan takara hudu dake neman shugabancin kungiyar tarayyar Turai a karo na farko, sun fara tafka wata mahawara a jami’ar Maastricht dake kasar Hollande, yayin da ya rage sauran makwanni hudu a gudanar da zaben.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Mahawarar wacce ake haskawa ta kafar telebijin, da nufin shawo kan masu zabe kimanin miliyan 400 na nahiyar ta Turai, na faruwa ne a dai dai lokacin da yankin ke fuskantar barazanar tsaro dangane da rikicin kasar Ukraine.
Rahotanni sun nua cewa muhimmai daga cikin batutuwan da ake mahawarar akai sun hada da batun tsaro, tattalin arziki da kuma ci gaban yankin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu