Turkiyya
‘Yan bindiga sun sace wasu matukan jirgin Turkiya
Wasu ‘Yan bindiga sun yi garkuwa da wasu matukan jirgin Tukiya guda biyu a yau Juma’a a kasar Lebenon. Ministan cikin gidan lebenon Marwan Charbel ya shaidawa kamfanin dillacin labaran Faransa cewa an yi garkuwa da matukan ne akan hanyarsu zuwa tashar jirgin birnin Beirut da misalin karfe uku na dare, Kuma wata majiya tace ‘yan bindiga hudu ne suka yi garkuwa da mutanen.
Wallafawa ranar:
Talla
Gwamnatin Turkiya ta yi Allah waddai da lamarin kuma ta bukaci ‘Yan kasarta su fice daga Lebenon saboda rikicin Syria da ya shafi kasar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu