Faransa
Hollande zai kai ziyara Algeria domin dinke barakar da ke tsakaninsu
Shugaban kasar Faransa Francois Hollande zai nufi zuwa kasar Algeria domin dinke barakar da ke tsakanin kasashen biyu tare da neman goyon bayan mahukuntan kasar su amince da daukar matakn soji a kasar Mali. Ana sa ran shugaba Hollande zai gana da shugaban Algeria Abdelaziz Bouteflika a dai dai lokacin da kasar ke yin bukin cika shekaru 50 da samun ‘yancin kai daga turawan Faransa.
Wallafawa ranar: