Isa ga babban shafi
EU-Girka

Shugabannin Turai za su yi kokarin hana Girka ficewa euro

Shugabannin kasashen Turai sun ce za su yi kokarin hana kasar Girka ficewa daga cikin kungiyarsu masu amfani da kudin euro tare da kare matakan tsuke bakin aljihu bayan Shugabannin sun gana a birnin Brussels  

Shugaban kasar Faransa Nicolas Sarkozy da Shugabar gwamnatin Jamus Chancellor Angela Merkel
Shugaban kasar Faransa Nicolas Sarkozy da Shugabar gwamnatin Jamus Chancellor Angela Merkel
Talla

Wasu manyan jami’an hukumar kungiyar kasashen Turai sun bukaci shugabannin kasashen samar da wani tsari idan Girka ta fice euro.

Bayan kwashe tsawon sa’o’I Shida shugabannin na ganawa a birnin Brussels, sun ce zasu yi kokarin Girka bata fice daga kungiyar euro ba.

“ Muna bukatar Girka a euro, amma muna bukatar kasar ta cim ma bukatun da ta amince da su”. Inji shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel.

Akwai dai sabanin ra’ayi tsakanin Faransa da Jamus tun bayan da Hollande ya gaji Sarkozy a matsayin Shugaban Faransa.

Akwai yiyuwar Girka za ta fice euro idan al’ummar kasar suka kada kuri’ar kin amincewa da tallafin kasashen Turai a ranar 17 ga watan yuni.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.