Har yanzu 'yan gudun hijira na fargabar komawa garuruwansu a Najeriya
Wallafawa ranar:
Kunna - 09:47
'Yan gudun hijira, musamman a arewa maso gabashin najeriya na cikin fargabar komawa kauyukan su, yayin da hare-haren masu dauke da makamai ke kara kamari a sassan kasar.
Yanzu haka dai mayakan jihadi sun bazu a sassan kasar, sabanin a baya da suka fi gudanar da ayyukan su a arewa maso gabas.
Lamuran tsaro kamar yadda masana suka tabbatar, na ci gaba da tabarbarewa a Najeriya, lamarin da ya jefa galibin al'ummar kasar cikin zulumi.
Latsa alamar sauti domin sauraron cikakken shirin da Shamsiyya Haruna ta shirya kan wannan al'amari.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu