Muhallinka Rayuwarka
Koma bayan da manoman Najeriya suka samu a kakkar girbi na Shekara ta 2023
Wallafawa ranar:
Kunna - 19:59
Shirin a wannan karo zaiyi dubi ne akan wasu bayanan kididdiga da suka yi nuni da cewa kakar noma ta shekara ta 2023, na daga cikin lokaci mafi muni ga mafi yawan manoman Nigeria a sakamakon matsalar sauyin yanayi da ta haifar da karancin ruwan sama.A halin yanzu dai, wata babbar kungiyar kasa da kasa mai suna Action Aid, ta bayyana cewa irin hasarar da manoman Nigeria suka dibga a bana ta haura Nera Trilion 3, a daidai lokacin da ake fama da tsadar kayan abinci a kasar.