Mu Zagaya Duniya
Bitar labaran mako- Yadda Sojin Najeriya suka yi hobbasa a yaki da ‘yan ta’adda
Wallafawa ranar:
Kunna - 18:51
A cikin shirin ‘Mu Zagaya Duniya’ mai bitar wasu daga cikin muhimman labaran, da suka fi daukar hankali a makon da ya kare sojin saman Najeriya sun halaka ‘yan ta’adda da dama yayin hare-haren da suka kaddamar kansu a jihohin Kaduna da Neja, sai Afghanistan, inda kungiyar Taliban ta cika shekara guda cif da sake kwace iko da mulkin kasar, bayan shafe shekaru 20 tana gwabza yaki da dakarun Amurka.