Isa ga babban shafi
Kasuwanci

'Yan Najeriya na cikin matsin tattalin arziki tun bayan janye tallafin mai

Wallafawa ranar:

Shirin 'Kasuwa Akai Miki Dole na wannan makon tare da Ahmed Abba ya mayar da hankali ne kan hauhawar farashin kayyaki da ake fama da shi a Najeriya, wanda ya jefa al'umma masu karamin karfi cikin halin kunci.

Wani sashe na ’yan tumatir da ke kasuwar Mile 12
Wani sashe na ’yan tumatir da ke kasuwar Mile 12 Aminiya
Talla

A Najeriyar tun bayan janye tallafin man fetir da kuma matsalolin rashin kudaden waje masamman dalar Amurka sun tsunduma kasar cikin mummunar hauhawar farashin kayayyaki a kasuwanni, lamarin da ya jefa al’ummar kasar musamman masu karamin karfi cikin mawuyacin hali.

Alkaluman hukumar kididdigar Najeriya na watan Satumba sun nuna cewa hauhawan farashin kayayyaki ya kai kashi 26.72, wanda masana ke gargadin zai iya kaiwa da kaso 30 cikin 100 nan da watan Disamba muddun ba’a kai ga gano bakin zarenba.

Domin duba girman matsalar hauhawan farashin, RFI Hausa ya leka kasuwar Mile 12 International dake birnin Legas, daya daga cikin manyan kasuwannin kayan abinci da gwari a kasar.

Mile 12 international market in Lagos --Nigeria
Mile 12 international market in Lagos --Nigeria © RFI Hausa

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Sauran kashi-kashi
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.