Isa ga babban shafi
Bakonmu a Yau

Dakta Abba Sadiq mazaunin Faransa kan zanga-zangar da ke faruwa a kasar

Wallafawa ranar:

An samu saukin tarzomar da dubban Faransawa ke yi, bayan shafe kwanaki 6, suna zanga-zangar da ta kazance, biyo bayan kashe matashi da wani jami’in dan sanda ya yi. Tun daga ranar Larabar da ta gabata ne dai aka fara samun sassaucin tashin hankalin, inda kididdiga ta nuna cewar mutane 150 jami’an tsaro suka cafke, sabanin masu  zanga-zanga sama da 700 da aka a ranar Asabar. 

An samu saukin tarzomar da dubban Faransawa ke yi, bayan shafe kwanaki 6.
An samu saukin tarzomar da dubban Faransawa ke yi, bayan shafe kwanaki 6. REUTERS - NACHO DOCE
Talla

Bayanai sun ce motoci sama da dubu 2 masu tarzomar suka kone a Faransa, tare da lalata gine-gine sama da 500. 

Kan wannan zanga-zanga da wasu lamuranna da suka shafe ta Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Abba Sadiq mazaunin kasar ta Faransa. 

Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar tattaunawar......

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Sauran kashi-kashi
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.