Isa ga babban shafi

Zanga-zangar Faransa: Magadan Gari sun yi bore

Magadan Gari a Faransa sun yi wani zama domin nuna adawa da zanga-zangar da aka shafe tsawon mako guda ana gudanarwa biyo bayan kisan gillar da wani dan sanda ya yi wa matashin nan mai suna Nahel, dan shekaru 17.

Wasu daga cikin Magadan Garin Faransa kenan da suka yi zanga-zangar adawa da harin da ake kai wa jami'an gwamnati.
Wasu daga cikin Magadan Garin Faransa kenan da suka yi zanga-zangar adawa da harin da ake kai wa jami'an gwamnati. REUTERS - STEPHANIE LECOCQ
Talla

Bayanai na nuni da cewa, zanga-zangar ta soma  lafawa bayan da gwamnatin Faransar ta matsa kaimi wajen dakile masu boren da suka yi ta kone-kone da fashe-fashen shaguna.

A yau Litinin da aka shiga rana ta shiga da gudanar da zanga-zanga, Magadan Garin Faransa sun yi kira ga al’ummar kasar da su koma kan turbar mutanta dokoki bayan da masu zanga-zangar suka kaddamar da hari kan gidan wani Magajin Gari a daura da birnin Paris.

Yanzu haka dimbin jama’a ne suka fito a yau domin nuna goyon bayansu ga Magadan Garin da sauran gwamnatocin kananan hukumomi da ake kai musu farmaki da sunan zanga-zangar.

A kokarinta na magance daya daga cikin manyan kalubalen da shugaba Emmanuel Macron ke fuskanta a gwamnatinsa, Ma’aikatar Harkokin Cikin Gidan Faransa ta girke jami’an ‘yan sanda dubu 45 da suka hada da jandarmomi a dukkanin fadin Faransa a cikin daren da ya gabata.

Yau ne dai masu bincike na cikin gida suka fara gudanar da bincike kan yadda dan sandan ya dirka wa Nahel harsashi a daidai lokacin da yake tukin mota ba tare da lasisi ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.