Bakonmu a Yau
Alhaji Sule Ammani Yari Katsina kan gargadin INEC na yiwuwar dage zabe a Najeriya
Wallafawa ranar:
Kunna - 02:53
A Najeriya, yayinda ‘yan siyasa ke ci gaba da karade sassan kasar domin fara zawarcin kuri’un jama’a, hukumar zabe a kasar INEC ta ce akwai yiyuwar matsalar tsaro da ake fama da ita ta sa a jinkirta gudanar da zaben ko kuma gaza gudanar da shi a wasu yankuna. To sai dai Alhaji Sule Ammani Yari Katsina, wanda ke bin diddigin lamurran da suka shafi siyasa da kuma sha’anin tsaro a kasar, ya ce hukumar zabe ba za ta iya daukar wannan mataki ba tare da shawarar hukumomin tsaro na kasar ba. Ga dai zantawarsu da Abdoulkarim Ibrahim Shikal