Bakonmu a Yau
Muhammad Magaji kan shirin gwamnati na daina sassautawa kamfanonin karkara
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:21
A Najeriya, wasu bayanai na nuni da cewa gwamnatin Tarayyar kasar na shirin kawo karshen sassaucin biyan haraji da ta ke yi wa kamfanonin da ke gudanar da ayyukansu a karkara. Wannan mataki dai na kunshe ne a cikin sabuwar dokar kasafin kudi, wanda yanzu haka majalisar ke yi wa gyara kuma ake kyautata zaton cewa za a amince da ita a cikin wannan mako. Kan hakan Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Muhammad Magaji, Sakataren yada labarai na kungiyar manoman Najeriya.