Bakonmu a Yau
Tattaunawa da Dr Tukur Mamu game da farmakin gidan yarin Kuje
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:25
Guda cikin shiga tsakani don ceto fasinjin jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna da ‘yan bindiga suka sace ya ce akwai alaka tsakanin wadanda suka farmaki gidan yarin Kuje da wadanda ke rike da fasinjan. Dr Tukur Mamu, wanda ya fara da bayani kan halin da Fasinjan ke ciki a yanzu haka, ya ce ‘yan bindigar sun yi barazanar farmakar gidan yarin matukar ba a saki 'yan uwansu da ke tsare ba. ga dai tattaunawarsa da Aminu Sani Sado.