'Yan bindiga sun kai hari kan gidan yarin Kuje
Hukumar kula da gidajen yarin Najeriya ta tabbatar da cewa ‘yan bindiga sun kaiwa cibiyarta ta kula da gyaran hali dake karamar hukumar Kuje a Abuja, babban birnin tarayya.
Wallafawa ranar:
Cikin sanrwar da ya fitar da safiyar yau Laraba, mai magana da yawun hukumar Umar Abubakar, ya ce hadin gwiwar jami’ansu dake dauke da makamai tare da wasu jami’an tsaro sun samu nasarar tarwatsa maharan da suka kaddamar da farmakin.
Zuwa lokacin wallafa wannan labari dai babu karin bayani kan adadin mutanen da suka jikkata ko kuma suka rasa rayukansu yayin harin da aka kaiwa gidan yarin na Kuje dake Abuja.
Sai dai kakin hukumar kula da gidajen yarin Najeriya ya ce za su fitar da karin bayanai kan lamarin a nan gaba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu