Tattaunawa da Malam Nasir Kura kan bukatar murabus din Buhari
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:36
Akalla Kungiyoyin fararen hula 127 da ke Najeriya ne suka bukaci shugaban kasa Muhammadu Buhari da ya gaggauta kawo karshen kashe kashe da zub da jinin da ake samu a kasar ko kuma ya sauka daga mukamin sa domin ceto kasar daga rugujewa.
Wata sanarwar hadin gwiwa da kungiyoyin suka sanya hannu ta ce a watanni 3 na farkon wannan shekara Najeriya ta ga tashin hankalin da ta dade bata gani ba abinda ya yi sanadiyar kashe akalla mutane dubu 2.
Dangane da wannan sanarwar Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Malam Nasir Kura na kungiyar Civil Liberty, kuma ga yadda zantawar su ta gudana.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu