Isa ga babban shafi
Nijar-'Yan ta'adda

Nijar ta fara shirye-shiryen neman sulhu da 'yan ta'adda

Jamhuriyar Nijar na shirin tattaunawa da ‘yan ta’adda masu ikirarin jihadi, wadanda hare haren da suke kaiwa a kudu maso yammacin kasar  suka girgiza ta.

Mohamed Bazoum, shugaban Nijar.
Mohamed Bazoum, shugaban Nijar. © Issouf SANOGO AFP
Talla

 

Kasar da ke yankin Sahel na fargabar yadda ‘yan ta’addan suka  sabanta hare hare a yankin Tillaberi tun bayan da Faransa ta sanar da cewa dakarunta za su bar kasar Mali.

Wata majiya daga ofishin shugaba Bazoum Mohamed  ta ce a watanni uku da suka wuce ne dai shugaban kasar ya tuntubi matasa da kungiyar IS ta yammacin Afrika ta dauka aiki a game da batun sulhu.

Majiyar ta ce shugaba Bazoum ya aike da manzanni don ganawa da wasu shugabannin ‘yan ta’adda 9.

A ‘yan kwanakin da suka wuce ne dai shugaba Bazoum ya saki ‘yan ta’adda da dama daga gidan yari, har ma ya karbi bakuncinsu a fadar  gwamnatin kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.