Gwamnatin Nijar ta tura karin sojoji Banibangou
Gwamnatin jamhuriyar Nijar ta ce an tura karin sojoji don tabbatar da tsaro a yankin Banibangou, bayan da ‘yan bindiga suka kashe fararen hula 66 kamar yadda sabbin alkaluma suka nuna, wadanda suka dawo daga cin kasuwa a ranar litinin da ta gabata.
Wallafawa ranar:
Ministan cikin gidan kasar Alkache Alhada, wanda ya ziyarci garin na Banibangou don jajantawa jama’a dangane da mummunan hari, y ace jami’an tsaron da aka tura za su rika zagayawa a cikin kauyuka da kuma kasuwanni domin kare rayuka da kuma dukiyoyin jama’a.
Ministan cikin gidan ya ce nan ba da jimawa za a tura karin jami’an tsaro 500, wadanda ke gab da kammala samun horo.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu