Isa ga babban shafi
Niger

Kotu a Niger ta Amince ayi Zabe Ba tare da katin shaida ba

Babbar kotun kasar Niger yau asabar ta zartas da hukunci don barin mutane marasa takardun shaida, wato ID Card  su jefa kuri'arsu a babban zaben kasar da za'ayi a  lahadi. 

Mutane na kallon hotunan 'yan takara da za su tsaya zaben lahadi
Mutane na kallon hotunan 'yan takara da za su tsaya zaben lahadi BOUREIMA HAMA / AFP
Talla

Gwamnatin Niger ta nemi a bar jama'a su jefa kuria idan  basu da takardun shaida,  muddin suna da wadanda za su iya gane su cewa 'yan kasa ne da suka cancanci jefa kuria.

‘Yan adawa ne suka soki wannan mataki, amma kuma kotun tsarin mulkin kasar, ta kawar da bukatar ‘yan adawan, kamar dai yadda Kadri Umaru Sanda, mutun na biyu a Hukumar Zabe mai zaman kanta a kasar ya sanar.

 

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.