Isa ga babban shafi

'Yan ta'adda sun yi wa tawagar jami'an tsaron gwamnan Yobe kwanton bauna

Wasu da ake zargi mayakan  Boko Haram ne sun yi wa tawagar jami’an tsaron gwamnan jihar Yobe  Mai Mala Buni kwanton bauna a wannan Asabar, lamarin da ya yi sanadin mutuwar dan sanda guda tare da jikkata 6.

Wata bindiga mai daukar alburusai 50.
Wata bindiga mai daukar alburusai 50. AFP - STEFAN HEUNIS
Talla

Lamarin ya auku ne a kan babban titin Jakana zuwa Mainok na jihar Borno a arewa maso gabashin Najeriya. Sai dai gwamnan ba ya tareda su a lokacin harin.

Tawagar jami’an tsaron sun yi wa gwamnan rakiya ne  zuwa bikin yaye daliban jami’ar Maiduguri da ke jihar ta Borno, inda aka karrama mataimakin shugaban Najeriya, Kashim Shettima da digirin girmamawa.

Kakakin gwamnan Yobe, Mamman Mohammed, ya tabbatar da aukuwar lamarin.

Mohammed ya  ce su ma ‘yan sandan ba su yi kasa a gwiwa ba a lokacin da suka fada cikin tarkon da ‘yan ta’adan suka dana musu, saboda  sun mayar da martani ta wajen bude wuta, amma duk da haka suka rasa mutum guda, wasu 3 suka jikkata.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.