Isa ga babban shafi

An kafa dokar hana fita ta sa'o'i 24 a Kano

Rundunar ‘yan sanda ta kafa dokar hana fita ta sa’o’i 24 a Kano, matakin da ta dauka, sa’o’i bayan da kotun sauraron kararrakin zaben jihar ta yanke hukuncin kwace kujerar Gwamna daga Abba Kabir Yusuf na jam’iyyar NNPP ta kuma mika ta ga Nasiru Yusuf Gawuna na APC.

Wani yanki na jihar Kano.
Wani yanki na jihar Kano. © Daily Trust
Talla

Ana dai kyautata zaton cewar an dauki matakin dokar hana fitar ne domin dakile duk wani yunkuri na yiwuwar tayar da zaune tsaye a sassan jihar ta Kano saboda hukuncin kotun.

Cikin sanarwar da ya rattaba wa hannu da kansa, Kwamishinan ‘Yan Sandan Kano, Muhammad Usaini Gumel, ya bayyana baza jami’an tsaro zuwa sassan jihar domin tabbatar da aikin dokar hana fitar.

Bayanai sun ce tuni mutane suka kauracewa ci gaba da gudanar da hada-hada a titunan birnin na Kano, yayin da a kafafen sada zumunta jama’a ke fadin albarkacin bakinsu kan hukuncin kotun sauraron kararrakin zaben na mika wa Nasiru Yusuf Gawuna kujerar gwamnan jihar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.