Isa ga babban shafi
Kano

Kotu ta mika wa Gawuna kujerar gwamnan jihar Kano

Kotun sauraren korafe-korafen zaben gwamnan Kano ta yanke hukuncin kwace nasarar da Gwamna Abba Kabir ya samu a zaben da ya gabata, inda ta bayyana Nasiru Gawuna a matsayin wanda ya lashe zaben.

Nasiru Yusuf Gawuna na jam'iyyar APC da kotun sauraron kararrakin zaben Kano ta mika wa kujerar gwamnan Jihar, bayan kwacewa daga Abba Kabir Yusuf na NNPP.
Nasiru Yusuf Gawuna na jam'iyyar APC da kotun sauraron kararrakin zaben Kano ta mika wa kujerar gwamnan Jihar, bayan kwacewa daga Abba Kabir Yusuf na NNPP. © Daily Trust
Talla

A yayin da take yanke hukuncin, Mai Shari'a Oluyemi Akintan ta ce bisa dogaro da haramcin wasu kuri'u sama da dubu dari da sittin da biyar, ta soke nasarar ta Abba Gida Gida tare da umartar hukumar zabe wato INEC da ta mika takardun nasara ga Dakta Gawuna.

Daga Kano wakilinmu Abubakar Isa Dandago ya aiko mana da rahoto kan halin da ake ciki.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.