'Yan Najeriya sun bayyana matsalolin da suke so Tinubu ya magance
Yayin da ya rage kasa da mako guda a rantsar da sabon shugaban Najeriya, ‘yan kasar sun bayyana matsalolin da suke son sabuwar gwamnatin ta fara magancewa daga cikin manyan matsalolin da suka addabi kasa
Wallafawa ranar:
Kunna - 01:26
Najeriya dai na daga cikin kasashen yammacin Afirka da ke fama da rikicin mayakan Boko Haram, da suka tilastawa miliyoyin mutane barin gidajensu, da kuma sanadiyyar rasa rayukan dubbai.
Bugu da kari kasar na fama da kalubalen masu garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa, a arewa maso yammada, sai kuma masu rajin kafa 'yantacciyar kasar Biafara wato kungiyar IPOB kenan a kudancin kasar.
Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken rahoton da Isma'il Karatu Abdullahi ya gabatar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu